Tuesday, September 14, 2010

WANI YA KASHE KANSA A KATSINA SABODA KUNSHI RAYUWA

Wani Yaro dan shekaru ashirin da biayr mai suna Muntari Ibrahim da ke zaune a unguwar tashar gagare cikin garin katsina ya rataye kansa inda nan take ya mutu.
A wata wasika day a bari kuwa jami’in yada labarai na rundunar ‘Yan Sanda a jihar katsina ya nunawa manema labarai, Marigayi Muntari y ace ya dau wannan matakin ne domin yagaji da halin da yake ciki.
Marigayi Muntari ya kuma roki gafarr Iyayensa, ya kuma fada cewa akwai wani dinkinsa wajen wani taila idan an amsu to a baiwa mahaifinsa.
Mahaifin nasa Ibrahim ya fadawa wakilinmu cewa wani Yaro ne dai ya leka dakin kofar gida a inda ya ga Muntari a rataye nan take ya sanar da mahaifinsa shi kuma ya fadawa ‘Yan Sanda.
Alhaji Ibrahim wanda yake malamin makarantar All one y ace marigayi masanin Qur’ani ne kuma Yaro ne natsustse.
Ya ce marigayi ya dauki tsawon shekaru biyar bashi gida, inda bai dade da dawowa ba.
A cewar uban Yaro ya dawo gida cikin koshin lafiya, inda babu wata alama ta motsuwa a jikin sa, ko alamun yana shaye-shaye ko wani abu na damunsa.
Safiyar da zai rataye kansa said a ya zo dakin ya gaida ni, inji uban Yaron.
Jami’an ‘Yan Sanda ne suka cire igiyar day a rataye kansa sannan suka kai gawar Asibiti a inda likita ya tabbatar da mutuwarsa.s

Thursday, August 19, 2010

KTSU MAIN GATE

YAR'ADUA VERSITY EMBARKED STRIKE IN KATSINA

The academic Staff union of Universities of the Umaru musa Yar’adua University katsina state has commenced a two week warning strike to actualise their demand for increase in salary.
The Chairman of the union,comrade Usman Abdullahi stated this while addressing a press conference in katsina.
Comrade Usman abdullahi said upto now the state government has refused to pay adequate attention to their demand which compelled the union to commence the warning strike today.
He said the union resolved to pursue for the full implementation of ASUU and FGN agreement in the instutition.
Comrade Usman abdullahi said going by the terms of employement between the state government and the member of the union as well as the benchmark for establishing a university in Nigeria as approved by the federal government, the union has categorically rejected the persistence of the state government to partially and unilaterally implement the FGN and ASUU agreement without recourse to laws of katsina state that was tantamount to the breach of the employement contract and violation of the laws of katsina state.
Comrade Usman Abdullahi called on the state government to fully implement the said agreement effective from july 2009.
All efforts to get the special adviser to the governor on Higher Education, Alh Adamu Mato Zango who was sighted by the reporters refused to comment, who later use the backdoor of his office and left the reporters stranded only to be told by the public Relation Officer that the adviser will invite them later for briefing on the state government’s position on the strike action.

HOTON ALH SABO MUSA KATSINA

MARTANIN DA ALH SABO MUSA YA MAYAR MA 'YAN CPC A KATSINA

wannan ita ce tattaunawar da wakilinmu da ke katsina ya yi da shugaban kungiyar tuntuba akan sake tsayawa takarar Gwamnan jihar katsina Barista Ibrahim Shehu Shema a katsina.
Alh. Sabo Musa yana daga cikin manyan 'yan siyasar jihar katsina yanzu,ya fadi dalilin kafa wannan kungiya ta so mai suna Shema partinership, sannan ya maida martanin akan zargin da jam'iyyar CPC ke yiwa Sarakunan katsina da jam'iyyar ta CPC ta ce sun atsoma baki cikin al'ammuran siyasar katsina, dama wasu bayanan ga yadda hirar take:
KH:Sabo musa kayi man bayani dalilin kafa wannan kungiya ta ku da kake yi wa jagoranci. Wanda kuma an kafa ta ne domin a ga gwamna Shema ya sake cin zabe a shekarar 2011?
SABO MUSA: gaskiya kamar yadda ka sani makasudin kafa wannan kungiya don mu sakawa shi gwamna, bisa ayyukan alherin da yake gabatrwa a jihar ta katsina. Ya kamat duk wani mai kiyasa a katsina, yasan irin abin da Shema ya yi wannan ne yasa muka hadu muka kafa wannan kungiya domin yin wani abu da zai nuna masa cewa mu mutanan katsina mun ji dadin abin da ya yi. Sannan mun lura gwamnati tana aiki amma mafi yawancin mutane ba son abin da ake ciki ba.
Dalili ba biyu shi ne akwai wasu 'yan mara sa kishi duk da cewa sun shiga gwamnati sun tara kudi, amma kuma ba su son irin abin da shi gwamna shema yake a karkashin gwamnantin shi saboda hassada, suna ganin su yakamata ace suke yi kuma ba su ke yi ba. Sai suka rika amfani da dukiyar suna haddasa fitinu. Wannan yasa duk lokaci da suka soke shi mu rama idan sukai masa sharri mu nunwa jama'a wannan abun ba haka yake ga yadda yake.
Abu na uka kuma shi ne, za mu son ya cigaba da zama gwamnan jihar katsina, idan aka samu can jin gwamnati mun shiga cikin wani irin hali, saboda irin abin da ya yi ba a taba samun gwamnan da ya iske aiki sai da ya ida sannan ya cigaba da na shi, ka ga hanyoyi da ya fara yin wadanda za su kewaye gari, ga kuma gidaje da ya gina idan har aka samun can jin gwamnati ana iya kashe irin wadannan manyan ayyuka. Bayan haka ga wasu ayyukan wadanda suna da matukar amfani ga jama'a, misali kamar Asibitin Turai yar'duwa da kuma Asibitin Kashi wanda masana suka ce duk Afrika babu irin ta, ga motocin tafi da gidanka wanda da amurika da finafinai kadai muke ganin su, hatta mutanan da ke cikin karkara suna afmana da wannan garabasa.
KH: To, amma sai gashi wasu 'yan siyasa suna ganin abun ba haka ne ba, ya yarda wasu 'yan siyasar da aka fara tafiya tare, wanda har wasu daga ciki suka fice daga PDP zuwa ta jam'iyya?
SABO MUSA: Wannan ba gaskiya ba ne, yau idan an kyautatama al'ummar jihar katsina ba a kyautatama wasu da ke tare da gwamnati ba anyi laifi? Saboda haka ita gwamnati ta al'ummar jihar katsina ce baki daya, tunda gwamnati ta al'ummar jiahar katsina ce idan aka kyautattawa wani ba a kyautattawa wani ba, ba a laifi ba. Wadanda suka bar jam'iyyar PDP suka kuma wata daman ba su yi ma jam'iyyar komi, duk wanda ke cikin PDP yake ya da manufar ta ba wata bukata tashi ta kashin kansa ba yana nan bai bar PDP ba.
KH: Gashi jam'iyyar CPC na zargin Sakunan katsina da tsuma baki cikin al'ammuran siyasa, musamman akwai wani sarki da ya nuna jam'iyyar da yake wane martani za ka maida akan wannan?
SABO MUSA: Ace Sarakunan mu suna jam'iyyu wannan cin mutunci masarautar mu ne da Sarakunan mu, wannan cin fuska ne ya kamata a daina. Sarakuna iyayen kasa ne, ra'ayi kuwa duk dan adam yana da na shi, yana son wane ya ci zabe, yana son wane saboda ayyukan alherin da yake ya zarce, saboda haka ra'ayi da ban siyasa da ban. Yau idan iyayen Sarakuna ba su ce Shema ya kyauta ba ai masu yi masa adalci ba, saboda ya kyauta din ya fito da mutuncin jihar katsina, ba a taba taimakon alhazai yadda ya kamata ba sai lokacin Shema, ba wata gwamnatin da ta taba gina masalatai da makarantu da kewaye makabarto ba kamar Shema, wannan aikin Sarakuna ne to sai gwamnati ta zo tana yin wannan don mi ba za su yabawa wannan gwamnati ba. Sannan ina kira ga kungiyar ma'aikata kadda su yarda ayi amfani da su, ko ace su nemi karin albashi, ko karin karamar hukuma ko neman jiha, sannan kadda a cuci ma'aikata amma kuma kadda su kuma su matsa su ce kan su suke so. Kamar ma'aikatan Asibiti da suka tafi yajin aikin ai ba su yi mutunci ba, ina kira a gare su da suji tsoron Allah shi aiki ba ana yin ba ne don albashi kawai, ana yin sa don taimako da samun lada. Saboda haka wancan kiraye-kiraye na CPC wannan abin je farwa ne, babu hujja babu ma'ana.
KH: To a karshe wane kira za kayi ga 'ya 'yam Jam'iyyar PDP su ga sun hada kawunan su domin gwagwarmaya mai zuwa a wannan zaben?
SABO MUSA: Mu 'yan jam'iyyar PDP kan mu hade yake, daman wadanda suke gefe suna ganin abin alheri ne garesu akafa wata gwamnati ai sun sa irin abin da suka aikata a kafa gwamnati su gani mana, yau mutanan nan duk abin da muke cikin gwamnatin nan da su muke ba su taba cewa PDP bata da gaskiya ba, sai yanzu ne za su zo su fadi yanzu ne PDP ba ta yi gaskiya? Bayan sun shiga gwamnati sun debi kudin jama'a to su maido ma gwamnati kudin ta mana, kuma ka tuba ba za kara yin abu be shi ne sharadin tuba, idan kuma kudi ne na wasu ka diba to ka maida masu kudin su sannan ka tuba. Saboda haka a karshe ina kira ga jama'ar jihar katsina gwamna shema ya yiwa mutane abin da ya da ce, mu fito mu saka mashi, duk farfaganda da wasu mutane keyi ku auna nagartar wadanda suka fito takara a wasu jam'iyyun ku gani mana, kuma sai ma ranar zabe za a kara ganin bambamcin shema da sauran.

HIRAR MASARI AKAN KOMARWARSA CPC A KATSINA

KH: A da kana jam'iyyar PDP wanda kuma kana da matukar tasiri, sai gashi lokaci guda ka kuma CPC babu shakka ba za ka rasa dalili ba?
MASARI: To da farko dai kamar yadda jam'iyar PDP ta gudanar da zaben ta a 2006 ta kuma fitar da 'yan takarar ta duk kasar Najeriya, yadda kuma sauran jam'iyyu suka bi sawun yadda jam'iyyar PDP ta yi na kama karya. Bayan mun sauka muka ce to ya kamata mu bullo da wata hanya wadda za ta gyara tsarin mulki da zai fidda zababu bi sa ka'ida, har ma akwai wata kungiya da muka kafa G20. To mun yi kokari a wannan lokacin manyan ta matsa har aka zo aka yi convension har aka gyara wasu al'amurra na tsarin mulki wanda za su fitar da ciyaman na kwamitin amintattu.
To amma wadanda suka amshi mulki sai suka fi da lalacewa, a hankali- ahankali tun wurin zaben muka ga abinda ba su mukayi tsammani ba, bayan an aje akwatina sai daga baya aka ce wai anyi yarjejeniya duk sun ci ni kuma na san zaben shugaban kasa kan shi ko mutun daya ne ya fito sai an je fasa kuri'a idan ku ce ba su san shi to dole a canza dan takara amma wannan karan a jam'iyyar PDP mai mako ta bada mafita sai ya kasance ita ce ma matsalar, sai ka ga gwamnoni sun dauke aikin jam'iayya, idan gwamnoni suka fito suka ce zasu yi kaza sanna sai shugabanin jam'iyyar PDP su ce to, sai ya kasance wutsiya ita ke kada kare ba kare ne ke kada wutsaya ba.
KH: Yanzu idan na fahimce ka, dalilin da yasa kuka bar wannan jam'iyyar kamar kuna babu adalci acikinta ne yasa kuka barta?
MASARI:Absolute. Duk hanyoyin da muka bi wanda zai kawo tsarin da zai yi adalci acikin maganar na karshen nan shi ne wanda muka kawo sauran gwamnoni da yaran su da ke c ikin jam'iyyra suka watsar, kuma ya kasance nine gaba-gaba wajen wannan gyara, gyara bai yi nasara ba, shi ya sa nayi abin da ya dace dole idan da zan bar PDP ne saboda abinda aka yi min da na bari tun shekara hudu da suka wuce, amma ban bari ba.
KH: Amma me yasa ka zabi komawa jam'iyyar CPC duk da cewar akwai wasu jam'iyyun da dama?
MASARI: Ita jam'iyyar CPC wadanda suka kafa ta, irin matsalolin da muka fuskanta a jam'iyyar PDP suma irinta suka fuskanta a jam'iyyar su suka bar ta suka kafa CPC mai akida, wanda kuma mu akidar muke son a bi, saboda haka idan ace ga ka'idar jam'iyya na bi, aka zo akayi jarabawa a matsayin 'yan takara ni da kai, ta nuna jama'a sun fin sonka shi kenan sai in mara maka baya, ai daman ga ka'idar, amma da rana kiri-kira aka baka kuma daga baya ace in zo in bika ai abin ya zama bauta kuma ni na gaji da ita.
KH: Amma gashi ita wannan jam'iya sabuwar jam'iyyar ce, ka na ganin alamun zata yi tasiri a siyasar Najeriya?
MASARI: Ba yawan jama'a sune kasuwa ba? Kai ka ga taron da akayi anan, ka ga motoci da mutanan da suka zo tunda daga sabuwa har Mai'adua, ka gani ko? Indai ba PDP za ta yi kwace ba, kuma a wannan karon ka ji abin da mutane suka ce sai dai akwata bisa ran su.
KH: Misali yanzu kana da wani ra'ayi na tsayawa takara, ko ba ka kai ga yanke shawara ba?
MASARI: Gaskiya yanzu ban yanke wata shawarar tsayawa takara ba.