Tuesday, September 14, 2010

WANI YA KASHE KANSA A KATSINA SABODA KUNSHI RAYUWA

Wani Yaro dan shekaru ashirin da biayr mai suna Muntari Ibrahim da ke zaune a unguwar tashar gagare cikin garin katsina ya rataye kansa inda nan take ya mutu.
A wata wasika day a bari kuwa jami’in yada labarai na rundunar ‘Yan Sanda a jihar katsina ya nunawa manema labarai, Marigayi Muntari y ace ya dau wannan matakin ne domin yagaji da halin da yake ciki.
Marigayi Muntari ya kuma roki gafarr Iyayensa, ya kuma fada cewa akwai wani dinkinsa wajen wani taila idan an amsu to a baiwa mahaifinsa.
Mahaifin nasa Ibrahim ya fadawa wakilinmu cewa wani Yaro ne dai ya leka dakin kofar gida a inda ya ga Muntari a rataye nan take ya sanar da mahaifinsa shi kuma ya fadawa ‘Yan Sanda.
Alhaji Ibrahim wanda yake malamin makarantar All one y ace marigayi masanin Qur’ani ne kuma Yaro ne natsustse.
Ya ce marigayi ya dauki tsawon shekaru biyar bashi gida, inda bai dade da dawowa ba.
A cewar uban Yaro ya dawo gida cikin koshin lafiya, inda babu wata alama ta motsuwa a jikin sa, ko alamun yana shaye-shaye ko wani abu na damunsa.
Safiyar da zai rataye kansa said a ya zo dakin ya gaida ni, inji uban Yaron.
Jami’an ‘Yan Sanda ne suka cire igiyar day a rataye kansa sannan suka kai gawar Asibiti a inda likita ya tabbatar da mutuwarsa.s

Thursday, August 19, 2010

KTSU MAIN GATE

YAR'ADUA VERSITY EMBARKED STRIKE IN KATSINA

The academic Staff union of Universities of the Umaru musa Yar’adua University katsina state has commenced a two week warning strike to actualise their demand for increase in salary.
The Chairman of the union,comrade Usman Abdullahi stated this while addressing a press conference in katsina.
Comrade Usman abdullahi said upto now the state government has refused to pay adequate attention to their demand which compelled the union to commence the warning strike today.
He said the union resolved to pursue for the full implementation of ASUU and FGN agreement in the instutition.
Comrade Usman abdullahi said going by the terms of employement between the state government and the member of the union as well as the benchmark for establishing a university in Nigeria as approved by the federal government, the union has categorically rejected the persistence of the state government to partially and unilaterally implement the FGN and ASUU agreement without recourse to laws of katsina state that was tantamount to the breach of the employement contract and violation of the laws of katsina state.
Comrade Usman Abdullahi called on the state government to fully implement the said agreement effective from july 2009.
All efforts to get the special adviser to the governor on Higher Education, Alh Adamu Mato Zango who was sighted by the reporters refused to comment, who later use the backdoor of his office and left the reporters stranded only to be told by the public Relation Officer that the adviser will invite them later for briefing on the state government’s position on the strike action.

HOTON ALH SABO MUSA KATSINA

MARTANIN DA ALH SABO MUSA YA MAYAR MA 'YAN CPC A KATSINA

wannan ita ce tattaunawar da wakilinmu da ke katsina ya yi da shugaban kungiyar tuntuba akan sake tsayawa takarar Gwamnan jihar katsina Barista Ibrahim Shehu Shema a katsina.
Alh. Sabo Musa yana daga cikin manyan 'yan siyasar jihar katsina yanzu,ya fadi dalilin kafa wannan kungiya ta so mai suna Shema partinership, sannan ya maida martanin akan zargin da jam'iyyar CPC ke yiwa Sarakunan katsina da jam'iyyar ta CPC ta ce sun atsoma baki cikin al'ammuran siyasar katsina, dama wasu bayanan ga yadda hirar take:
KH:Sabo musa kayi man bayani dalilin kafa wannan kungiya ta ku da kake yi wa jagoranci. Wanda kuma an kafa ta ne domin a ga gwamna Shema ya sake cin zabe a shekarar 2011?
SABO MUSA: gaskiya kamar yadda ka sani makasudin kafa wannan kungiya don mu sakawa shi gwamna, bisa ayyukan alherin da yake gabatrwa a jihar ta katsina. Ya kamat duk wani mai kiyasa a katsina, yasan irin abin da Shema ya yi wannan ne yasa muka hadu muka kafa wannan kungiya domin yin wani abu da zai nuna masa cewa mu mutanan katsina mun ji dadin abin da ya yi. Sannan mun lura gwamnati tana aiki amma mafi yawancin mutane ba son abin da ake ciki ba.
Dalili ba biyu shi ne akwai wasu 'yan mara sa kishi duk da cewa sun shiga gwamnati sun tara kudi, amma kuma ba su son irin abin da shi gwamna shema yake a karkashin gwamnantin shi saboda hassada, suna ganin su yakamata ace suke yi kuma ba su ke yi ba. Sai suka rika amfani da dukiyar suna haddasa fitinu. Wannan yasa duk lokaci da suka soke shi mu rama idan sukai masa sharri mu nunwa jama'a wannan abun ba haka yake ga yadda yake.
Abu na uka kuma shi ne, za mu son ya cigaba da zama gwamnan jihar katsina, idan aka samu can jin gwamnati mun shiga cikin wani irin hali, saboda irin abin da ya yi ba a taba samun gwamnan da ya iske aiki sai da ya ida sannan ya cigaba da na shi, ka ga hanyoyi da ya fara yin wadanda za su kewaye gari, ga kuma gidaje da ya gina idan har aka samun can jin gwamnati ana iya kashe irin wadannan manyan ayyuka. Bayan haka ga wasu ayyukan wadanda suna da matukar amfani ga jama'a, misali kamar Asibitin Turai yar'duwa da kuma Asibitin Kashi wanda masana suka ce duk Afrika babu irin ta, ga motocin tafi da gidanka wanda da amurika da finafinai kadai muke ganin su, hatta mutanan da ke cikin karkara suna afmana da wannan garabasa.
KH: To, amma sai gashi wasu 'yan siyasa suna ganin abun ba haka ne ba, ya yarda wasu 'yan siyasar da aka fara tafiya tare, wanda har wasu daga ciki suka fice daga PDP zuwa ta jam'iyya?
SABO MUSA: Wannan ba gaskiya ba ne, yau idan an kyautatama al'ummar jihar katsina ba a kyautatama wasu da ke tare da gwamnati ba anyi laifi? Saboda haka ita gwamnati ta al'ummar jihar katsina ce baki daya, tunda gwamnati ta al'ummar jiahar katsina ce idan aka kyautattawa wani ba a kyautattawa wani ba, ba a laifi ba. Wadanda suka bar jam'iyyar PDP suka kuma wata daman ba su yi ma jam'iyyar komi, duk wanda ke cikin PDP yake ya da manufar ta ba wata bukata tashi ta kashin kansa ba yana nan bai bar PDP ba.
KH: Gashi jam'iyyar CPC na zargin Sakunan katsina da tsuma baki cikin al'ammuran siyasa, musamman akwai wani sarki da ya nuna jam'iyyar da yake wane martani za ka maida akan wannan?
SABO MUSA: Ace Sarakunan mu suna jam'iyyu wannan cin mutunci masarautar mu ne da Sarakunan mu, wannan cin fuska ne ya kamata a daina. Sarakuna iyayen kasa ne, ra'ayi kuwa duk dan adam yana da na shi, yana son wane ya ci zabe, yana son wane saboda ayyukan alherin da yake ya zarce, saboda haka ra'ayi da ban siyasa da ban. Yau idan iyayen Sarakuna ba su ce Shema ya kyauta ba ai masu yi masa adalci ba, saboda ya kyauta din ya fito da mutuncin jihar katsina, ba a taba taimakon alhazai yadda ya kamata ba sai lokacin Shema, ba wata gwamnatin da ta taba gina masalatai da makarantu da kewaye makabarto ba kamar Shema, wannan aikin Sarakuna ne to sai gwamnati ta zo tana yin wannan don mi ba za su yabawa wannan gwamnati ba. Sannan ina kira ga kungiyar ma'aikata kadda su yarda ayi amfani da su, ko ace su nemi karin albashi, ko karin karamar hukuma ko neman jiha, sannan kadda a cuci ma'aikata amma kuma kadda su kuma su matsa su ce kan su suke so. Kamar ma'aikatan Asibiti da suka tafi yajin aikin ai ba su yi mutunci ba, ina kira a gare su da suji tsoron Allah shi aiki ba ana yin ba ne don albashi kawai, ana yin sa don taimako da samun lada. Saboda haka wancan kiraye-kiraye na CPC wannan abin je farwa ne, babu hujja babu ma'ana.
KH: To a karshe wane kira za kayi ga 'ya 'yam Jam'iyyar PDP su ga sun hada kawunan su domin gwagwarmaya mai zuwa a wannan zaben?
SABO MUSA: Mu 'yan jam'iyyar PDP kan mu hade yake, daman wadanda suke gefe suna ganin abin alheri ne garesu akafa wata gwamnati ai sun sa irin abin da suka aikata a kafa gwamnati su gani mana, yau mutanan nan duk abin da muke cikin gwamnatin nan da su muke ba su taba cewa PDP bata da gaskiya ba, sai yanzu ne za su zo su fadi yanzu ne PDP ba ta yi gaskiya? Bayan sun shiga gwamnati sun debi kudin jama'a to su maido ma gwamnati kudin ta mana, kuma ka tuba ba za kara yin abu be shi ne sharadin tuba, idan kuma kudi ne na wasu ka diba to ka maida masu kudin su sannan ka tuba. Saboda haka a karshe ina kira ga jama'ar jihar katsina gwamna shema ya yiwa mutane abin da ya da ce, mu fito mu saka mashi, duk farfaganda da wasu mutane keyi ku auna nagartar wadanda suka fito takara a wasu jam'iyyun ku gani mana, kuma sai ma ranar zabe za a kara ganin bambamcin shema da sauran.

HIRAR MASARI AKAN KOMARWARSA CPC A KATSINA

KH: A da kana jam'iyyar PDP wanda kuma kana da matukar tasiri, sai gashi lokaci guda ka kuma CPC babu shakka ba za ka rasa dalili ba?
MASARI: To da farko dai kamar yadda jam'iyar PDP ta gudanar da zaben ta a 2006 ta kuma fitar da 'yan takarar ta duk kasar Najeriya, yadda kuma sauran jam'iyyu suka bi sawun yadda jam'iyyar PDP ta yi na kama karya. Bayan mun sauka muka ce to ya kamata mu bullo da wata hanya wadda za ta gyara tsarin mulki da zai fidda zababu bi sa ka'ida, har ma akwai wata kungiya da muka kafa G20. To mun yi kokari a wannan lokacin manyan ta matsa har aka zo aka yi convension har aka gyara wasu al'amurra na tsarin mulki wanda za su fitar da ciyaman na kwamitin amintattu.
To amma wadanda suka amshi mulki sai suka fi da lalacewa, a hankali- ahankali tun wurin zaben muka ga abinda ba su mukayi tsammani ba, bayan an aje akwatina sai daga baya aka ce wai anyi yarjejeniya duk sun ci ni kuma na san zaben shugaban kasa kan shi ko mutun daya ne ya fito sai an je fasa kuri'a idan ku ce ba su san shi to dole a canza dan takara amma wannan karan a jam'iyyar PDP mai mako ta bada mafita sai ya kasance ita ce ma matsalar, sai ka ga gwamnoni sun dauke aikin jam'iayya, idan gwamnoni suka fito suka ce zasu yi kaza sanna sai shugabanin jam'iyyar PDP su ce to, sai ya kasance wutsiya ita ke kada kare ba kare ne ke kada wutsaya ba.
KH: Yanzu idan na fahimce ka, dalilin da yasa kuka bar wannan jam'iyyar kamar kuna babu adalci acikinta ne yasa kuka barta?
MASARI:Absolute. Duk hanyoyin da muka bi wanda zai kawo tsarin da zai yi adalci acikin maganar na karshen nan shi ne wanda muka kawo sauran gwamnoni da yaran su da ke c ikin jam'iyyra suka watsar, kuma ya kasance nine gaba-gaba wajen wannan gyara, gyara bai yi nasara ba, shi ya sa nayi abin da ya dace dole idan da zan bar PDP ne saboda abinda aka yi min da na bari tun shekara hudu da suka wuce, amma ban bari ba.
KH: Amma me yasa ka zabi komawa jam'iyyar CPC duk da cewar akwai wasu jam'iyyun da dama?
MASARI: Ita jam'iyyar CPC wadanda suka kafa ta, irin matsalolin da muka fuskanta a jam'iyyar PDP suma irinta suka fuskanta a jam'iyyar su suka bar ta suka kafa CPC mai akida, wanda kuma mu akidar muke son a bi, saboda haka idan ace ga ka'idar jam'iyya na bi, aka zo akayi jarabawa a matsayin 'yan takara ni da kai, ta nuna jama'a sun fin sonka shi kenan sai in mara maka baya, ai daman ga ka'idar, amma da rana kiri-kira aka baka kuma daga baya ace in zo in bika ai abin ya zama bauta kuma ni na gaji da ita.
KH: Amma gashi ita wannan jam'iya sabuwar jam'iyyar ce, ka na ganin alamun zata yi tasiri a siyasar Najeriya?
MASARI: Ba yawan jama'a sune kasuwa ba? Kai ka ga taron da akayi anan, ka ga motoci da mutanan da suka zo tunda daga sabuwa har Mai'adua, ka gani ko? Indai ba PDP za ta yi kwace ba, kuma a wannan karon ka ji abin da mutane suka ce sai dai akwata bisa ran su.
KH: Misali yanzu kana da wani ra'ayi na tsayawa takara, ko ba ka kai ga yanke shawara ba?
MASARI: Gaskiya yanzu ban yanke wata shawarar tsayawa takara ba.

HOTON DAKTA MUSTAPHA INUWA

TATTAUNAWAR MU DA DAKTA MUSTAPHA INUWA, TSOHON SAKATAREN GWMANTIN JIHAR KATSINA AKAN KOMAWARSA CPC

Tambaya: Dakta Mustapha da farko za mu so muji dalilin ficewarka daga jam'iyyar PDP?
DAKTA: To, dalilin dai kamar yadda muka sha fada wurare daban-daban shi ne rashin adalci da gwamnan jihar katsina Ibrahim Shehu Shema da makarabansa suke yi, a yadda suke tafiyar da harkokin jam'iyya da ita kanta gwmanatin jihar katsina.
Jam'iyya dai ya kamata ace ta kowa-da-kowa ce shi yasa ake ce mata PDP power, amma sai muka ga an maida Shema political Party saboda an zo an zauna duk wani wanda yana da hannu wajen haihuwar jam'iyyar da kuma raya ta ta hanyoyi da dama daga 1998 zuwa yau amma Shema ya zo ya nuna baya bukatar shi ya jawo wasu mutane ya ce sune za su? tafiyar da harkokin siyasa. Ya zo ya rushe kwamitin zartarwa na jam'iyya tun daga matakin gunduma har zuwa jaha, ya na da wadanda ya ga dama acikin ofis din shi, to wanna yasa muka nuna ba mu yarda ba, ba taimako bane ga jam'iyya, a rushe ayi kamar yadda doka ta tsara, sannan muka bi duk matakin da ya kamata mu bi anan jiha muka kai koke tarayya, daga karshe ta tabbata ba, sai muka fahimce Shema nema yake ya kashe jam'iyyar PDP mu kuma ba za mu so a kashe ta ba muna ciki.
Dalili na biyu shi ne ita dai jam'iyya amfanin ta idan an kafa gwamnati to ta taimaka ma jama'a, musamman alkawarin da aka dauka lokacin zabe, da dama Shema muka zagaya muka roki jama'a domin a zabe shi za a yi masu ayyuka na alheri, wadanda suka shafi kowane bangare, sai mu ka ga shi Shema ba wannan ya da me shi ba sai manyan ayyuka musamman hanyoyi har da inda ba a bukatar hanya.
An bar mutane babu ruwan sha, babu magani, makarntu daliban sun koma almajirai, an ki daukar malamai, musamman na karkara an sa kananan hukumomi sun gina an ki daukar ma'aikata, sai mu ka ga babu dalilin da sai sa mu ba wannan gwamnati goyan baya, to sai muka bai kamata ba mu cigaba da zama cikin wannan jam'iyya saboda babu wani aiki da a ka yi wa jama'a ba re aba da misali da shi har a sake zabar ita wannan jam'iyya, to wannan da ma wasu dalilai da dama ya sa muka fita daga PDP.
TAMBAYA: Ba ka gani irin manyan ayyukan da ya yi kamar yadda kace; kamar hanyoyi da gidaje da ya yi wanda har ana ta bashi kyaututika, ba ka ganin wannan nasara ce wanda kuna iya duba al'amarin?
DAKTA: Su wa? Wadanda suka san matsalolin mutanan katsina koko? Wadanda suke bada irin wadannan kyaututikan idan ka bincika ba wanda ya taba zuwa katsina, wadannan kyaututinkan biya ake ana bada so da daman su, kuma kyautar da ya amsa ta farko ba ta aikin sa ba ce, akin da mukayi ne na farko domin an bata ta ne 2006 ba ta shi ba ce ya karba amma daga lokacin zuwa yanzu wace kyauta ya karba? Amma a zahiri mutanan da ke katsina su suka son halin da ake ciki, yanzu idan ka je asibiti ba magani lokacin gwamnatin da ta shude ana sayen magani na Naira miliyan dari hudu, amma yanzu na miliyan arba'in ake saye, gashi ba ruwan sha ba a dauke ma'aikata aiki ba.
Ga shi kananan hukumomi ba sa iya komin sai abinda gwamnatin jiha ta ce masu, komi Ciyaman zai yi sai ya neman izini a jiha kuma daga can za a bashi dan kwangilar da zai yi aikin, amma maida kusan mutun biyu sune ke yin kwangilar ayyukan kananan hukumomin jihar katsina, magana ce ta gaskiya sai dai mutane ba su son a fadi domin tsoro ko wani dalili, ko su Ciyamomin tsakani da Allah ba su jin dadin wannan gwamnati suke ji ba, an maida kamar almajirai saboda babu wani aiki da suke, kuma za ka ga kananan hukumomi suna samun kudin da basu kasawa miliyan ashirin ba bayan sun biya albashi amma me ake da su? Dan abin da za a ba su daman da ta so kishirwar sun wawure. Maganar ace ana bashi award a je 'yan Abuja su zabe shi, idan kuma maganar zabe ne kai ka sani mutane sun gaji da gwamnatin shehu ba za su sake zaban ta ba.
TAMBAYA: To, mutane da yawa suna ganin shigowar ku CPC ya yi za kuyi ku amshi wannan gwamnati?
DAKTA: To, ba jama'a ke zabe ba? Insha'Allahu jama'a za su zabe gwamnatin CPC kuma ba wai jihar katsina kadan ba, daman su ke zabe.
TAMBAYA:Kana ganin yanayin zaben zai canza ganin yadda ake zabe a baya?
DAKTA: Karma ya canza, mutane su za su canza shi da kan su, ace wai anyi sabuwar doka duk wannan ba shi bane, in jama'a na son su ci zabe za su ci, ai anyi anan jihar ba wainsaia anje nisa ba, anan katsina 2003 anyin zabe mun fadi, Sanatoci biyu muka rasa cikin uku, 'yan majalisa takwas muka rasa cikin sha biyar, inda zaben farko aka fara anan jihar na gwamna Umaru da baiyi second term ba, kuma wahalar da mutane suke cikin yanzu ita ta sa suka ce ko za su mutu sai dai mutun amma sai sun tsare mutuncin su a wannan karon daga wannan wulakantatar gwamnati.
TAMBAYA: A karshe wane kira za ka yi ga masu ruwa da tsaki da hukumomin tsaro da kuma ita kanta hukumar zabe ta kasa domin tabbatar da anyi zabe cikin adalci da lumana?
DAKTA: Ni kira zanyi ga dukkan jama'a, musamman sakunan mu da suka zu bar ma kansu da mutunci, suna abinda yake mutane fa ba su jin dadin sa, ya kamata su tsare mutuncin su, su tsare girman su, su dauke kowa na su ne, duk wanda Allah yasa aka zaba to na su ne, amma ace sakuna suna bada umarni kiri-kiri suna ga ya ma jama'a ga gwamnatin da suke so, to wannan kuskure ne.
sannan akwai jami'an hukumar kananan hukumomi suna za ga yawa suna gaya wa mutane cewa duk wanda baya siyasar gwamnati to cire hula ya fi wahala akan korar sa daga aiki, to su kori duk wanda suke son su kori su gani ai in su jahilai ne ba su san dokokin kasa ba, tsarin mulki bai hana duk wani mutun ba ya fadi ra'ayin sa ba. Kumu su jami'an tsaro da ka ce, a Najeriya ta yanzu zaman lafiyar su ne su bar jama'a su zabi wanda suke so ayi abin cikin adalci da kwanciyar hankali, babu jami'an tsaron da ke iya hana fitinar da za ta zo ida har aka samu wani abu akasin haka. Sannan babu hukumar zaben da ke iya hana jama'a su zabi wanda suke so, kuma idan har suka ce za su lalata abin da akayi to abinda zai biyu baya ba zai yi ma mutane kyau ba.

Friday, August 13, 2010

NAN KUMA MONDAY NE RIKE DA BIBLE ACIKIN MASALACI

GA SHI NAN A TATTARO MASA KAYAN SA DA KE CIKIN MASALACI ZUWA...

LABARIN MAYAUDARIN KIRISTA A KATSINA

Daga: Abdulkwanarya
A ranar Lahadi 8/8/2010 ne asirin wani mutum da ya musulunta a masallacin kungiyar Izala da aka fi sani da Kandahar Kofar Kaura Katsina tsawon shekara uku da ta gabata mai suna Monday wanda ya canja suna zuwa Ahmad ya tonu, bayan da ya safe shekaru ukun yana yaudarar masu kula da wannan masallaci ta hanyar karbar tallafi.
Yadda abin ya faru kuwa shine, wani dan acaba (kabu-kabu) ne ya dauko Monday daga wata Coci ya kawo shi wannan masallaci.Bayan ya ajiye shi ne, sai ya ga wannan mutum ya shige cikin masallaci, abinda ya cikashi da mamakin da ya kasa daurewa har sai da ya tambaya kodai akwai hanyar bi-ka-wuce ta wannan masallaci. an ba hi amsa da cewa babu wata hanya, masallaci ne kawai.sannan ya tabbatar masu da cewa ya fa dauko wani mutum daga Coci ya kawo shi nan kuma lallai yana nan cikin masallacin.Sai aka shiga da wannan dan acaba , ya kuma nuna Monday cikin masallacin gaban kayansa da dama anan cikin suke kuma nan yake kwana. A nan take aka caje shi ,sai aka sami wani Littafin da aka rubuta "Littafi mai Tsarki" akansa.
Yayin da aka tambayi Monday akan lamarin ya tabbatar da cewa, haka aka yi bai kuna musanta faruwar hakan ba sai dai ya ce, bai dade da komawa zuwa Cocin ba. An kuma tambaye shi mi yasa da ya koma Kiristansa bai bar masallacin ba? Sai ya yi shiru babu amsar da ta fito daga bakinsa.
Bayan musuluntar Monday, "har makaranta aka sama masa a Kaduna , amma ya ki ya halarta"inji Ustazu Sani Musa, a lokacin da yake kara bayani akan lamarin.
An yi kokarin mika Monday ga hukumar tsaron farin kaya,amma suka ce a bayar da shi ga hukumar 'yansanda, za su karbi batun daga bisani.
Wani da wannan Dandali na katsinawahausawa ya nemi jin ta bakinsa akan wannan lamari, ya bayyana abin da cewa akwai sakaci da bangaren yan gunkiyar da har suka kyale wannan mutum tsawon wannan lokaci ba tare da bin diddikin wadanda yake mu'amala da su ba" mi ya hana su binciki shi kowanene, danginsa da makamantan su don su san dawa suke mu'amala"a tabakain wannan malami.
Shin Monday dan leken asiri ne na kungiyar kiristocin Nijeriya (CAN) ko kuwa dan leken asirin wasu kungiyoyin ne na daban? Kuma hukumomin tsaron za su iya yi wani abu akan lamarin ? Tambayoyin da har zuwa aiko da wannan labari ba a sami amsoshinsu ba.

Wednesday, July 21, 2010

BETWEEN SHEMA AND UMYU WHO WANTS TO KILL THE UMARU MUSA YAR’ADUA UNIVERSITY, KATSINA

As we know, the managing and sponsoring of any University, is not like other institutions; such as polytechnics and colleges of education. That is why it is being regarded as the most important aspect in all educational sectors particularly in katsina state, under the leadership of governor Ibrahim Shehu Shema. But what we believe is that the importance of University can not be over emphasized, because it is the one that produces good leaders who will move the nation in socio-economic and political direction.
The recent crisis and mis-understanding between Asuu Umaru Musa Yar'adua University katsina state chapter and Governor Ibrahim Shema over their allegation on agreement of the new salary structure has become a cut throat among themselves.
Similarly, it was in that controversial situation, after Asuu held a meeting released a communique that “katsina state government sponsored a tour to all 34 members of House of assembly to China without giving any reason for that tour” but House assembly denied that they were not sponsored by state government.
The union of this (UMYU) has been boiling out since the university claimed that, the katsina state government has not made any response about their demand almost ten months ago. Asuu organized a press conference with news men in katsina to indicate their stand over the issue that state government did not even consider. With saying “this implementation has already been approved by the federal government”
In the same vein, the special adviser on higher education of katsina state during a meeting both Asuu and state government, he lamented that the state government has already set-up a committee that gives the advice to resolve the matters, with the saying “ I assured that, the state government is fully aware about the issue and very soon will announce the stand”.
After a prolonged, yet state government did not any physical replayed from their own side. This was led an acute action taken by union of UMYU katsina state chapter to organize a second press conference with news men in the University compass.
The union warned the government about a problems that Umaru Musa Yar'adua University may face before October, 2010 include: 1 brain drain to other neighboring Nigerian University that are massively recruiting academic staff to meet the minimum NUC requirement for establishing a university. 2 risk of some departments in the university being shut down by forthcoming NUC accreditation team for not meeting the minimum staff NUC requirement to exist as accredited units of the university. My question to the state governor is, does he want these disasters that have already mentioned affect this university with his negligent?
The prompt replied by the katsina state government through special adviser on media and public relation Malam Nasir Abdul says “what UMYU Asuu did on the issue of implementation new salary structure it was totally wrong, to say government refused their demand after months in dialog”.
Here, our concern, both Asuu and state government who wants destroying Umaru Musa Yar'adua University in particular?
The whole staff and non-staff of the UMYU knew the history of established the university by the later President Alhaji Umaru Musa Yar'adua when he was a governor in katsina state.
Also the governor of katsina state knows the importance of educations and he has been proud the sector as priority, so we don't know which kind of play with part of people's life?
My advice to governor of katsina state, if he is taking this problem as menial thing, surely will led him to loss the katsina state gubernatorial election.
Mohammed Zaharadeen, katsina
08062212010/07027129735
mzaharadeen@yahoo.com
www.katsinahausawa.blogspot.com

Monday, July 12, 2010

HABA! AL-AMIN CIROMA

Daga Mohammed Zaharadeen, katsina
Batu akan badakalar ‘yan fim da Malam Rabo abu ne da babu ranar da za’a daina tattaunawa akan shi, musamman a kafafen watsa labarai, kuma tarihi ba zai taba mantawa da shi ba.
Haka kuma akwai masu goyon bayan ‘yan fim akan sana’ar su amma basu tare da su akan sauran ma’amullolinsu na yau da kullin, sannan akwai wadanda su a wajansu ‘yan fim akan kowane irin mataki ba masu laifi bane, kuma ba za su taba yin laifi ba. wasu kuma na ganin akwai inda yakamata a gyara. Haka abin yake idan aka juya akan Malam Rabo wasu na ganin da gangan ne gwamnatin jihar Kano ta kawo shi domin ya takurawa ‘yan fim da harkar baki daya. Idan kuma ka dubi wani bangaren za’a ga wasu suna goyon bayan irin matakin da hukumar tace finafinai ta jihar kano ta dauka akan ‘yan fim cewa daidai ne idan da abinda yafi haka a kara.
Wannan tasa babu wata rana da zata wuce ba’ace wani abu ba akan wannan batu ba, haka kuma abu ne da ba zai taba gushewa ba a zukatan mutane musamman wadanda suke sane da irin wainar da ake toyawa tsakanin ‘yan fim Malam Rabo.
Idan har ba nayi kuskure ba, akan wannan batu ne Malan Aminu Ciroma yake son mutane da kansu su gane inda matsala take tsakanin Malam Rabo da ‘yan Fim daga nan sai a san wace hanya za’abi domin warwareta, ina ganin haka Ciroma ke son fayyacewa masu karatu irin mu.
Akan rigimar ‘yan Fim da Malam Rabo, ni a wurina duk abinda za’ace akan Malam Rabo wallahi bai da me ni ba domin nasan Rabo ba kanwar lasa bane. Haka kuma duk abinda za’ace akan ‘yan fim bai da me niba saboda suma nasan ba kanwar lasa bane.
Amma abinda nake son yin magana akai shi ne gaskiyar magana tun lokacin da na karanta rubutun Ciroma na farko mai take “Rabo da ‘yan fim a mahangar Ilimi” wallahi naji wani shakku akan wannan rubutu domin gudun kadda ciroma yayi aikin da ba na shiba ya yanke hukunci, ma’ana kadda ya kwafsa, dalilin na jin wannan tsoro shi ne ciroma ba dan Jarida bane amma ma’aikacine a kamfanin buga jarida a fanbaran na’ura mai kwakwalwa (computer operator) duk da cewar yan cikin wannan masa’anta hakan ba zai hana shi amfani da basira, ilimi da kuma hikimar da Allah ya bashi wajan yin wannan nazira ba domin masalahar wannan masana’anta wadda hatta wadanda ba cikinta suke ba suna son ganin irin wannan badakala ta kawo karshe tsakanin ‘yan fim da Malam Rabo, amma matsalar itace da wahala ya iya kiyaye dokokin aikin jarida wajan rubuta irin wannan labarin wanda ina da tabbacin sai da yayi dogon bincike kafin ya zauna ya rubuta shi (writing the investigative report or write-up).
Duk da cewar bani da tabbas akan mutane biyun da suka yiwa ciroma wasu tambayoyi ko martani yana da nasaba da rashin tabbas din da suke da shi na ganin da wahala yayi abinda yakamata yayi, wanda hakan yasa suka kasa barinka har sai rubutub naka ya kare kafin nan sai su yi maka duk tambayar da zasu yi maka. Amma kuma idan da zaka bi ka’idar aikin jarida ni bani da matsala ko shakko akan cewa ba zakayi adalci ba, sai gashi wadannan mutane biyu sun yi maka ingiza mai kantu ruwa ka fadi matsayar akan harkar Fim da sunan bada amsa tun kafin rubutun naka ya kare, inda nan ne duk wani mai tambaya ko martani yake da damar yi maka kai kuma ka bashi amsa ba tare da kame-kame ba.
Maganar da kayi da sunan bada amsa ga tambayar zan kawo da kuma amsar da ka bada inda nan ne nake ganin ka kwafsa, “ shin su ‘yan fim ba su da laifi ne? Idan suna da shi, me yasa ba mu ji ka na yawan yi masu tambihi ba? Ko kuwa don ka na daga cikin masu shirya finafinan ne”? wannan itace daya daga cikin tambayoyin da aka yiwa ciroma. Shi kuma ga amsar da ya bada “game da me yasa bani farfagandar laifin ‘yan fim, sai in ce maka, wata kila yau ka fara karanta ni ko shafina a wannan jarida. Idan ba haka ba, to ya na da kyau, ka waiwaya baya, domin kuwa zan yi alfaharin cewa tun da na fara ta ba yin rubutu a fannin finafinan Hausa a wannan jaridar, ban taba nunuwa a fili cewa wai ‘yan fim ba su da laifi ba. Idan mai karatu na biye da wannan shafin, nake jin, babu wata jarida da ta bada labarin badakalar da Maryam Hiyana ta yi, kamar Leadership Hausa”. Wannan kusan ince shi ne jigon amsar da ya bada, amma daga karshe ne dadin labari ya kwashe shi yake cewa “Acikin ‘yan fim, wallahi, zan iya dafa Alqur’ani cewa mafi yawansu, ba su san abinda ake kira Luwadi ko Madigo ba, kuma ba sa shaye-shaye, sannan uwa uba, ba sa yin Zina”. Ciroma wannan furuci da kayi a wurina ka rusa duk abinda kake kokarin fitowa da shi a fili domin jama’a su gane tsakanin Malam Rabo da ‘yan Fim a ina matsalar take?
Al-amin kayi hakuri, zan yi maka wata matshiya da wasu abubuwa da suka faru a farfajiyar shirin fim wanda yana da wahala kace baka son sun faru ba, koda baka son duka ba nasan kasan wasu, wanda hakan ya su daga cikin ‘yan fim suka aikata yasa ake kallon su da kuma danganta su da shaye-shaye, Madigo, Luwadi da kuma Zina, wanda kai kayi ikirarin cewa zaka iya dafa Alqur’ani mafi yawan ‘yan fim ba su ma san abinda ake nufi da kalmomin da na ambata ba gami da su, wannan a fili yake ka nuna kai dai indai akan ‘yan fim ne, sai dai akashe tsohowa kan daddawarta.
Abubuwa guda goma da zan kawo a wannan rubutu nawa zasu yi maka manuniya akan ‘yan fim da zaka dafa Alqur’ani akan su, daga nan sai masu karatu su yanke hukunci akan lamari. Kayi hakuri Ciroma cewa mafi yawan su, ni dauka kashi 70% cikin dari, basu san abinda ake nufi da wadannan miyagun halaye ba, ban san inda kake wadannan abubuwan suka faru ba har baka sani ba kuma ba’a baka labari ba, ko wannan ya nuna cewa kai ba dan jarida bane, marubuci ne kawai? Matashiya akanka kafin in fara bayanin sauran, ina iya tuna lokacin da Mujallar fim ta buga hotonka kana ba wata yar fim abinci a lokashin wanda hakan yayi matukar taba mutuncinka, sannan da yawan mutanan da suka san akidarka duk da cewa ...kai akidar ma kwamashiyal ka keyi, in baka sani ba, to ka sani, suna cin mutuncin masu iri akidarka da bada misalin wannan hoton naka da aka buga, da fatan ka tuna da wannan.
1 Abu na farko shi ne, zan fara da misalin abinda ya faru a garin da nake wanda duk wanda yake harkar fim a katsina yasan wannan maganar. Akwai lokaci da marigayi Ahmed S. Nuhu suka zo shotin katsina wata yarinya daga cikin yan fim din tayi satar hanya taje ta kwana dakin wani saurayi, washegari da ta dawo ya kamata ya zane ba wanda ya bashi hakuri sai wanda bai san abinda ya faru ba, ba yan fim din katsina kadai ke wajan ba har da na Kano wanda nasan in daya daga cikinsu ya karanta wannan labari zai tuno da lokacin, haka itama yarinya duk da cewar yanzu ta girma a harkar da anyi maganar zata tuna. Tambaya anan me ake nufi da kwana dakin wanin saurayi da wannan yar fim tayi a katsina?
2 Abu na biyu shi ne wanda duk duniya ta san shi, shugabanninyan fim na Kano sukayi taro sukace sun tsaida mafi yawancin ‘yan fim sakamakon laifuffukan da ake zarginsu da aikatawa, laifuffukan sun hada da shaye-shaye, Madigo, Luwadi da kuma Zina. Haka kuma babu wani dan fim daga cikin wadanda aka tsaida da yace an bata masa suna ko anci mutuncinsa saboda haka yana neman hakkinsa a kotu. Tambaya anan ciroma yana nufin bai taba jin wannan labarin ba, duk da cewa jaridar da yake aikin tana daya daga cikin kafafen watsa labarai da ake dogaru da su?
3 Na uku shi ne, a Kano abin ya faru, marubuci Bala Makosa ya taba wani rubutu inda ya bayyana yadda ‘yan siyasa Malaman buge ke basu fatawar cewar idan har suna son biyan bukatar su to lallai sai sunyi Zina da fittaciyar ‘yan fim kafin bukata ta biya, Makosa ya bada hujja ne da cewar yan fim da abin ya faru da su ne suka bayana masa hakan. Tambaya anan ciroma bai taba jin wannan labarin ba? Inda yana da tababa ya tambayi Bala Makosa zai ji karin bayani.
4 Na hudu kuma, na taba kai ziyara ofishin wani mawalafin Mujalla a kaduna, muna cikin hira sai muka tabo maganr ‘yan fim, shi ne yake cewa, “ ni nasha fada cewa ‘yan fim ba za su iya kare kansu a waje na ba, bare a je wajan Allah sakamakon abubuwan da suke aikata” mai wannan maganar yasan harkar fim ciki da wajanta a duk fadin arewacin kasar nan. Daga nan yace “ka ga nan inda kake zaune”. Nace eh! To anan wata ‘yar fim ta zauna nake tambayarta ya sunan macen da bata kwana gidan iyayenta? Sai ta amsa da “mai dabi’ar karuwa” sai yace mata da yawan mata ‘yan fim haka suke, ya kara da cewa kuma bata yi gardama, sannan fitacciyar Jaruma ce ko wancen lokacin, kuma nasan da taga wannan rubutun zata iya tunawa. Anan me Ciroma zai ce akan wannan ‘yar tattaunawa?
5 Haka kuma akwai wata ‘yar wasa da take Kano da zama ana yi mata lakabi da ... ‘yar Madigo, kuma tana amsawa babu wanda ya taba cewa me yasa take amsawa, sunan ‘yar wasan ya fara kalma “Z” sannan ina da tabbacin cewa Ciroma yasan wannan yarinyar idan ma har bai santa ba, to ita ta sanshi kuma har yanzu tana cikin wannan masana’anta ana damawa da ita. Ina mai ba Ciroma tabbacin cewa idan yanzu ya hadu da wannan ‘yar wasa da ya kirata da wannan sunan zata amsa kamar yadda inda nace Al-amin Ciroma zai yi wuf ya amsa da cewa na’am.
6 Baya ga wannan a garin kaduna, acikin wata mujallar da ke bada labarin ‘yan fim suna Gidauniya Alhaji Yakubu Lere ya taba bada labarin cewa wata ‘yar wasa mai Suna Ismuha ta haukache sakamakon shan miyagun kwayoyin da take ba dare ba rana. Kuma wannan labarin babu wanda bai san shiba. Zanyi mamakin cewa Ciroma bai san da wannan labarin ba, alhali yana cikin garin kaduna.
7 Abu na bakwai shi ne, wata ‘yar wasan da yanzu idan aka lisafa jerin masu tashe to dole ta zama ta biyu ko ta uku, abu ya faru dasu ita da babbar aminiyarta a garin katsina, amma labarin ya cika garin Kano kamar can ne abin ya faru. Yadda abin ya faru duk shekara ‘yan fim sukan zo Gala katsina wannan ya basu damar ko ba gala ba sai su niki gari zuwa katsina domin shakatawa, suma wadannan aminnai guda biyu haka ta faru da su, a wani hotal da ake Kira Zanburush hotel da ke katsina, inda wasu daga cikin abokan sana’ar su suka kai masa ziyarar bazata suna bude dakin sai kawai aka gansu, daya saman daya kwanciyar mace da namiji, haka kuma kwanan nan mujallar fim ta kara bada labarin daya daga jarimar da abin ya faru da ita cewa ana zarginta da tara mata gidanta, amma sai ta bada wani dalili na zaman su gidan nata. Abinda ya faru a katsina yasa kungiyar masu shirya finafinai ta Moppan reshen jihar katsina ta raba wata takardar cewa ba yarda a kara ba wani dan fim koma daga ina yake masauki ba, har sai ta amince a kowane hotel da ke cikin garin katsina haka kuma masu hotal suka amince da wannan doka ta Moppan. Zan so Ciroma ya kara fadada yadda yake samun labarai gami da ‘yan fim daga ko’ina cikin fadin arewa domin kadda ya rika fakewa a garin kaduna da Abuja ya rubuta san ransa.
8 Na takwas shi ne , da wani babban yaron Maryam Hiyana ya fada cewa don me yasa aka dora karan tsana akan Maryam ita kadai, abinda tayi babu wata ‘yar fim da batayi hakan ba, ko don su ba’a dauka ba a waya ana turawa mutane? Kuma shi wanda yayi wannan maganar babu abinda za’a boye masa a wannan harkar domin da shi ake yinta tuntuni. Kuma ina da tabbabcin Ciroma yasan wannan yaron na Hiyana in kuma bai Sani ba ya tambayi masu aiko masa da labarai daga garin Kano domin cikeken bayani akan wannan furuci na shi.
9 Abu na tara wanda shi ne na kusa da na karshe cikin abubuwa goma da nace zan lissafa, kwanan nan ne mujallar fim ta buga wani labari wanda ina da yakinin Ciroma ya karanta in ma bai karanta ba wani ya bashi labarin, hukumar hada fatauci da shan miyagun kwayoyi ta kai wata ziyarar ba zata gidan ‘yar wasa Safiya Musa inda sukayi awan gaba da wasu daga cikin yaranta, wanda hakan ke nuna ko Safiya bata shaye-shaye tana daure wasu gindi suna yi.
10 Nagoma wanda shi ne duk lokacin da na tuna da shi sai naji cewa inda babu harkar fim da abinda ya samu wannan baiwar Allah da bai same ta ba. Wata ‘yar wasa da ake yiwa lakabi da “Beauty” wanda ina cewa kowa yasanta a harkar fim ta shaida mani cewa, babbar nadamarta a wannan harka shi ne tayi ciki kuma ta zubar da shi wannan al’amari yana matukar tada mata hankali a rayuwarta ta duniya kuma gashi bata san yadda zata yi ba tunda ta kashe rai. Wadannan abubuwan ba suke nan ba a’a na dai takaita su ne zuwa goma domin Ciroma ya kara samun haske akan tambayar da zan yi masa daga karshe akan furucin da yayi da dafa Alqur’ani akan ‘yan fim.
Ciroma wadannan abubuwan da na lissafa na daga abubuwan da mafi yawan jama’a suke dogaru da su wajan danganta ‘yan fim da wadancan miyagun halaye wanda kai kace kashi 70% ba su ma san abinda ake kira da wannan sunaye ba. Gaskiyar magana naga kuskuranka akan wannan furuci da kayi, domin ni a zatona ko Dictionary aka baka, ba zaka taba yarda ka dafa ka yi shaidar mutanan da ba kowane lokaci kake tare da su ba, amma ba zan yanke maka hukunci ba har sai ka amsa mani wadannan tambayoyi guda biyu.
1 Ciroma wane irin Alqur’ani ne zaka dafa akan cewar ‘yan fim kashi 70% basu ma san abinda ake zargin su da aikatawa ba? Duk da kace dafawa zakayi ba rantsewaba, ina ganin kamar baka san banbancin rantsuwa dafa Alqur’ani ba, shi Alqur’ani kana iya rantsewa da shi ko da baka taba shi ba ma damar kayi imani da shi ba sai ka dafa ba.
2 wadanne ‘yan fim ne zakayi rantsuwa akansu na Kano, Kaduna, Katsina koko ‘yan fim din Hausa baki daya?
Idan har kabani amsa akan wadannan tambayoyi to kana da uziri a wajena kuma zan goyi bayanka ka dafa Alqur’ani, shin dafawa ko rantsuwa? Daga karshe kuma in ka kammala da wannan rubutun naka mai taken “Rabo da ‘yan fim a mahangar Ilimi” abu na gaba da zakayi rubutu akan shi shine me yasa mutane suke yiwa ‘yan fim kudin goro? A maimakon idan mutun daya yayi laifi to abin ya tsaya kansa shi kadai maimakon ya shafawa sauran.
Daga Mohammed Zaharadeen, katsina
08062212010/07027129735
katsinawahausawa@yahoo.com
www.katsinawahausawa.blogspot.com